• Home  
  • Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasar Najeriya Ya Dawo Daga Ziyarar da Ya Kai Faransa
- Labarai

Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasar Najeriya Ya Dawo Daga Ziyarar da Ya Kai Faransa

Zaɓaɓɓen shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya dawo ƙasar nan bayan wata ziyara da ya kai ƙasar Faransa inda ya shafe tsawon mako biyar.

Zaɓaɓɓen shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya dawo ƙasar nan bayan wata ziyara da ya kai ƙasar Faransa inda ya shafe tsawon mako biyar.

A baya an bayyana cewa, dalilin tafiyar shi ne samun hutu bayan kammala yaƙin neman zaɓen da zaɓen da aka gudanar da ya tabbatar da shi a matsayin shugaban ƙasa mai jiran gado.

Tun farko an tsara cewa zaɓaɓɓen shugaban na Najeriya zai kwan biyu a Paris cikin ƙasar Faransa, daga nan kuma ya wuce zuwa birnin London, kafin ya dangana da ƙasar Saudiyya.

Sai dai rashin ganin sa a ƙasar Saudiyya lokacin aikin umrah, musamman daidai lokacin da shugaban ƙasar mai barin gado, Muhammadu Buhari yake can, ya haifar da jita-jita da raɗe-raɗi.

Tinubu ya sauka ne da yammacin a yau a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe, da ke Abuja babban birnin ƙasar nan.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000