Home » Ƙetare: Ƙasar Sin Ta Ƙara Kasafin Kudin da Take Kashewa a Fannin Tsaro

Ƙetare: Ƙasar Sin Ta Ƙara Kasafin Kudin da Take Kashewa a Fannin Tsaro

Kasashen Ƙetare

by Aishatu Sule
0 comment

A Lahadin nan China ta ce yawan kudin da take kashewa a fannin tsaro zai karu ainun a cikin shekaru 4 masu zuwa, tana mai kashedi a game da abin da ta kira da barazana daga waje.

Shugaban China Xi Jinping ne ya yi wannan bayani a wani taron majalisar dokokin kasar, a daidai lokacin da take daf da ba shi wa’adi na 3 a matsayin shugaban ƙasa.

Ga Wani Labarin: Adamawa: Ɗan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar LP Ya Janye Wa Aishatu Binani ta APC

Wani karin kasafi a bangaren tsaron ƙasar Sin shi ne mafi girma a duniya, kuma hakan na zuwa ne bayan da ƙasar ta sanar da ƙudirin bunƙasa tattalin arzikinta na kimanin kaso 5 a wannan shekarar.

A cikin kasafin kudin nata na wannan shekara, bangaren tsaro zai samu yuwan tiriliyan 1 da digo 55, kwataankwacin dalar Amurka biliyan 225, wato, ƙarin kaso 7 da ɗigo 2 kenan.

Sai dai har yanzu kasafin kuɗin bangaren tsaron na Sin ƙasa yake da Amurka, wadda ta ware dala biliyan ɗari 8 ga ɓangaren tsaro.

Sai dai wasu masana na ganin ƙasar ta Sin tana kashe sama da abin faɗa a hukumnance.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?