Home » Ɗangote Ya Rage Farashin Man Fetur Saboda Bukukuwan Ƙarshen Shekara 

Ɗangote Ya Rage Farashin Man Fetur Saboda Bukukuwan Ƙarshen Shekara 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Matatar Man Ɗangote a rage farashin man fetur zuwa N899.50k kan kowace lita albarkacin bukukuwan ƙarshen shekarar 2024. 

Babban jami’in kula da sa hannun jari da sadarwa na gamayyar kamfanonin Ɗangote Anthony Chiejina ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a safiyar ranar Alhamis.

Anthony Chiejina ya ce an dauki matakin ne don “sauƙaƙawa ‘yan Najeriya bukatun lokacin hutun ƙarshen shekara”.

Matatar man ta kuma nuna jin daɗin ta ga ‘yan Najeriya kan goyon bayan da su ke ba shi musamman lokacin da kasar ke shiga lokacin shagulgulan Kirsimeti da ƙarshen Shekara.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?