Home » An Sace Wayoyi Miliyan 25 A Cikin Shekara 1 A Najeriya – NBS

An Sace Wayoyi Miliyan 25 A Cikin Shekara 1 A Najeriya – NBS

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS), ta ce an sace wayoyin salula sama da miliyan 25, daga watan Maris ɗin 2023 zuwa Afrilun 2024.

NBS ta ce wannan sata ta shafi sama da mutum miliyan 17 a tsakanin wannan lokacin.

Ƙididdigar ta NBS na nufin cewa a cikin wayoyi 10 da mutane ke amfani da su, an sace guda bakwai a shekara guda.

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa ta kuma ce an fi samun satar wayoyin a gidaje da wuraren taruwar jama’a, kuma kashi 11.7 ne kacal na waɗanda aka yi wa satar suka kai wa ’yan sanda rahoto kuma suka samun taimakon da su ke nema.

Rahoton, ya kuma bayyana cewa ƙasa da kashi 10 na laifin satar wayoyi ne, suka kai gaban ’yan sanda, saboda dalilai daban-daban.

“A matakin ‘yan ƙasa kuwa, kashi 21.4 na ’yan Najeriya ne, suka ce an aikata musu laifin da ya saɓa wa doka, kuma satar waya na daga cikin manyan laifukan, inda yake da kashi 13.8,” in ji rahoton.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?