• Home  
  • An Sace Wayoyi Miliyan 25 A Cikin Shekara 1 A Najeriya – NBS
- Babban Labari - Labarai

An Sace Wayoyi Miliyan 25 A Cikin Shekara 1 A Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS), ta ce an sace wayoyin salula sama da miliyan 25, daga watan Maris ɗin 2023 zuwa Afrilun 2024.

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS), ta ce an sace wayoyin salula sama da miliyan 25, daga watan Maris ɗin 2023 zuwa Afrilun 2024.

NBS ta ce wannan sata ta shafi sama da mutum miliyan 17 a tsakanin wannan lokacin.

Ƙididdigar ta NBS na nufin cewa a cikin wayoyi 10 da mutane ke amfani da su, an sace guda bakwai a shekara guda.

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa ta kuma ce an fi samun satar wayoyin a gidaje da wuraren taruwar jama’a, kuma kashi 11.7 ne kacal na waɗanda aka yi wa satar suka kai wa ’yan sanda rahoto kuma suka samun taimakon da su ke nema.

Rahoton, ya kuma bayyana cewa ƙasa da kashi 10 na laifin satar wayoyi ne, suka kai gaban ’yan sanda, saboda dalilai daban-daban.

“A matakin ‘yan ƙasa kuwa, kashi 21.4 na ’yan Najeriya ne, suka ce an aikata musu laifin da ya saɓa wa doka, kuma satar waya na daga cikin manyan laifukan, inda yake da kashi 13.8,” in ji rahoton.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai