Ƙungiyar ‘Yan Jaridu Ta Ƙasa, NUJ, Ta Taya Sabon Hadimin Gwamnan Kano Murna

Ƙungiyar ‘Yan Jaridu ta ƙasa reshen jihar Kano ta taya sabon jami’in yaɗa labarai na gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf.

Sanarwar taya murnar wacce ta samu sa-hannu ciyaman ɗin ƙungiyar kwamared Abbas Ibrahim da sakataren ƙungiyar kwamared Abba Murtala waɗanda suka ce an ajiye ƙwarya a gurbinta saboda irin ƙwarewa da yake da ita.

Ƙungiyar ta yi wa Sunusi Bature Dawakin Tofa fatan zai gudanar da ayyukansa cikin nasara.

Post masu alaƙa

Babandede Ya Ziyarci Iyalan Hon. Laushi, Ya Ba Su Tallafi

Da Fulani Aka Kama da Wuraren ƙera Makamai a Filato, da War Haka Duniya ta Dauka:-Zagazola Makama

Gwamna Bala Mohammed ya canja sheka daga jam’iyar PDP zuwa jam’iyyar APM