Ambaliya Ta Karya Gada A Kasar Nijar

Daga Suraj Na Iya Idris Kududdufawa

Babbar gadar da ake shiga babban birnin Yamai a kasar Nijar ta karye sakamakon mamakon ruwa saman da ake yi samu a yankin. 

Gadar ta karye ne tsakanin mahadar jihar Doso da mahadar shiga birnin na Yamai.

Mafiya yawan al’ummar da suke bi ta jihar Doso domin shiga birnin sun hakura da shiga.

A yanzu dai haka akwai motocin matafiya a jibge a hanyar sakamakon wannan lamari da ya afku na karyewar gadar.

Akwai mutane daga jihoshi da dama a kasar Niger da sai sun bi ta jihar Doso sannan su isa birnin suma lamarin ya ritsa dasu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *