Home » Rundunar Civil Defence Ta Kama Gangar Man Fetur 150 a jihar Oyo

Rundunar Civil Defence Ta Kama Gangar Man Fetur 150 a jihar Oyo

Rundunar Civil Defence/Satar man Fetur

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Rundunar Civil Defence a Najeriya ta ce ta yi nasarar kama gangar man fetur 150 da aka yi safarsa da niyyar fitarwa daga ƙasar nan zuwa ƙasar Kamaru tare da wasu mutum biyu da ake zargi.

Babban kwamandan hukumar a jihar Akwa Ibom Yusuf Imam ne ya bayyana hakan a yau ga manema labarai a Oyo babban birnin jihar.

Imam ya ce sashen rundunar mai kula da gaɓar teku ne ya yi aiki da bayanan sirrin da ya samu na cewa wasu mutane ɗauke da man fetur a cikin kwale-kwalen katako na kan hanyar zuwa Kamaru.

Ya ƙara da cewa jami’an hukumar sun kuma ƙwace injina biyar tare da wani inji da ake amfani da shi wajen satar mai.

Imam ya kuma ƙara jan kunnen masu aikata irin waɗananna laifuka a gabar ruwa waɗanda ke yin ƙafar-ungulu ga tattalin arzikin ƙasar nan da cewa za su fuskanci mummunan hukunci.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?