• Home  
  • ‘Yan Sanda 272 Sun Samu Karin Girma A Kano
- Babban Labari - Labarai

‘Yan Sanda 272 Sun Samu Karin Girma A Kano

Rundunar ƴan sandan jihar Kano, ta yi bikin kara wa jami’an ta 272 girma, a matakai daban-daban kamar yadda hukumar kula da aiyukan yan sanda ta kasa PSC ta amince.

Daga Mujahid Wada Musa

Rundunar ƴan sandan jihar Kano, ta yi bikin kara wa jami’an ta 272 girma, a matakai daban-daban kamar yadda hukumar kula da aiyukan yan sanda ta kasa PSC ta amince.

An gudanar da bikin karin girman a wajen shakatawar manyan jami’an yan Sanda dake unguwar Bompai a ranar Litinin.

Kwamishinan yan sandan jihar Kano CP Salman Dogo Garba, ya taya wadanda suka samu karin girman, Inda yaja hankalin su kan ci gaba da jajircewa kan aikinsu.

Cikin wadanda likafar ta su ta daga sun hada da, mataimakan kwamishinan yan sanda 4, sai mutane 50 daga matakin SP zuwa CSP sai mutane 32 daga DSP matakin zuwa SP da kuma mutane 286 daga matakin ASP zuwa DSP.

Rundunar ta ce wannan rana ce ta farin ciki agare su, da wadanda suka samu karin girman da kuma iyalansu.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai