• Home  
  • Gwamnan Bauchi Ya Kara Nada Wa Kansa Mataimaka168
- Babban Labari - Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Kara Nada Wa Kansa Mataimaka168

Gwamnan jihar Bauchi Sanata Bala Abdulqadir Mohammed ya sanar da nadin karin wasu mataimaka na siyasa guda 168 da za su taimaka masa wajen tafiyar da jihar.

Gwamnan jihar Bauchi Sanata Bala Abdulqadir Mohammed ya sanar da nadin karin wasu mataimaka na siyasa guda 168 da za su taimaka masa wajen tafiyar da jihar.

Wannan na kunshe a cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai, Mukhtar Gidado ya fitar, Gwamna Bala Mohammed ya bayyana sabbin nade-naden mutane 168 da suka hada da manyan mataimaka na musamman, mataimaka na musamman.

Wadanda aka nada sun hada da manyan mataimaka na musamman guda biyar akan harkokin siyasa da al’umma, daya akan al’amuran fansho, mataimaka na musamman 60 da sauransu.

Gidado ya jaddada cewa an kafin a nadin, an dubi cancanta, ƙwarewa da gogewa, da kuma iya shugabancin waɗanda aka nada, domin da yawa daga cikinsu tsoffin jami’an siyasa ne.

Ya bayyana matakin an gwamnan jihar Bauchi a matsayin wani bangare na dabarun karfafa harkokin mulki, kara kawo hadin kai, da kuma karfafa hanyoyin samun nasarorin gwamnatin a ajihar.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai