Home » Ba Daidai Ba Ne Tinubu Ya Ci Gaba Da Ciyo Bashi Duk Da Cire Tallafin Mai – Sanusi

Ba Daidai Ba Ne Tinubu Ya Ci Gaba Da Ciyo Bashi Duk Da Cire Tallafin Mai – Sanusi

Sarkin Kano kuma tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Muhammadu Sanusi II, ya bai dace gwamnatin Shugaban Kasa Bola tinubu ta ci gaba da ciyo bashi ba

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Sarkin Kano kuma tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Muhammadu Sanusi II, ya ce  bai dace gwamnatin Shugaban Kasa Bola tinubu ta ci gaba da ciyo bashi ba bayan ta cire tallafin man fetur.

Yayin da yake jawabi a Abuja ranar Talata, a taron Oxford Global Think Tank Leadership da ƙaddamar da wani littafi, Sanusi ya ce cire tallafin man ya haifar da ƙaruwar kuɗaɗen shiga na gwamnati.

Sanusi ya kuma yaba wa gwamnatin Tinubu kan cire tallafin man fetur da daidaita farashin musayar kuɗi, yana mai bayyana matakan a matsayin “masu raɗaɗi amma na wajibi.”

Sai dai ya yi gargaɗin cewa waɗannan gyare-gyare ba za su yi tasiri ba sai an haɗa su da tsari mai kyau na kashe kuɗi da gaskiya a cikin gudanar da gwamnati.

“In ka daina biyan tallafi amma ka ci gaba da yin rance, hakan na nufin ka rufe rami guda ne sai ka buɗe wani. Kalubalen da ke gabanmu yanzu shi ne ingancin yadda gwamnati ke kashe kuɗi da kuma yadda ake tafiyar da kuɗaɗen da aka ce an ajiye,” in ji shi.

Sanusi, wanda ya jagoranci CBN daga 2009 zuwa 2014, ya ce matsalolin tattalin arzikin Najeriya a yanzu sun faru ne a sakamakon rashin daidaito a manufofi da siyasar neman sai an faranta wa jama’a da aka dade ana yi.

“A shekarar 2012, mun yi gargaɗin cewa tallafin mai ba zai dore ba, amma siyasa ta shigo. Yanzu, waɗanda suka jagoranci zanga-zangar adawa da cire tallafin su ne suka gaji matsalar, kuma ba su da wani zaɓi sai su yi abin da ya dace,” in ji shi.

Ya yaba wa ƙwararrun da ke cikin tawagar tattalin arzikin gwamnati kan matakan da suka ɗauka don daidaita hauhawar farashi da rage canjin farashin kuɗi, amma ya jaddada cewa dole ne a dakile ɓarna da almubazzaranci cikin gaggawa.

Yayin da yake tambaya kan yadda gwamnati ke kashe kuɗi, Sanusi ya ce: “Me ya sa muke da ministoci 48? Me ya sa ake da jerin motocin gwamnati masu yawa? Me ya sa har yanzu ana yin rance bayan cire tallafi? In ka rufe rami guda, me ya sa za ka buɗe wani?

“Wannan gwamnati na bukatar ta duba hukumomi da yadda ake amfani da kuɗi a dukkan matakai. Domin in ka ci gaba da samun kuɗi amma kana kashewa ba daidai ba, za ka lalata duk wani ci gaba da aka samu.

“Amma irin mu da za mu ce, ‘Ya Shugaban Ƙasa, wannan ba daidai ba ne,’ ana ɗaukarmu a matsayin abokan gaba. Don haka, idan shugabanni sun kewaye kansu da masu yabon kai, ba za su taɓa samun shawara mai kyau ba.

“Shi ya sa irin su Aigboje Aig-Imoukhuede da ni kan zama kamar abokan gaba ga gwamnati, domin mutane ba sa son jin gaskiya.”

Sanusi ya ƙara da cewa: “Mun faɗa wa Buhari komai, game da buga kuɗi, almubazzaranci, farashin musayar kuɗi da tallafi, amma duk lokacin da muka yi hakan, ana ɗauka a matsayin hari kai tsaye. Waɗanda ke kewaye da shi sun sa ya ɗauke mu a matsayin abokan gaba. Shugabanni dole su fara tambaya: wa nake kewaye da kaina da su?,” in ji Sanusi.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?