• Home  
  • An dakatar da shugaban NSCDC a Neja kan mutuwar masu haƙar ma’adanai 37
- Labarai

An dakatar da shugaban NSCDC a Neja kan mutuwar masu haƙar ma’adanai 37

Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin dakatar da shugaba hukumar tabbatar da tsaro da kare haƙƙin al’umma, NSCDC a jihar Neja, Suberu Aniviye, sakamakon mutuwar wasu matasa da ake zargin masu haƙar ma’adanai ne ta ɓarauniyar hanya. Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayar da umarnin a sanarwar da ya wallafa a shafinsa […]

Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin dakatar da shugaba hukumar tabbatar da tsaro da kare haƙƙin al’umma, NSCDC a jihar Neja, Suberu Aniviye, sakamakon mutuwar wasu matasa da ake zargin masu haƙar ma’adanai ne ta ɓarauniyar hanya.

Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayar da umarnin a sanarwar da ya wallafa a shafinsa na X inda kuma ya buƙaci a gudanar da cikakken bincike kan lamarin, da rahotanni ke cewa ya faru a yankin Wushishi/Lukoto da ke Mina, babban birnin jihar ta Neja.

A cewar sanarwar, an kama waɗanda ake zargi masu haƙar ma’adanai ne ba bisa ƙa’ida ba yayin samamen da aka kai a yankunan jihar a ranar Talata da kuma Laraba na wannan makon.

A cewar ministan, “muna tafiyar da gwamnati ce wadda babban abin da ta sa a gaba shi ne kare rayukan jama’a kuma muna aiki tuƙuru don tabbatar da hakan”.

Ya kuma buƙaci jama’a da su kwantar da hankalinsu sannan u ci gaba da kasancewa masu bin doka da oda.

Tun da farko, gwamnan jihar Neja ta ce an kama kwamandan hukumar.

Jam’ian hukumar da ke yankin Borgu a jihar sun kama matasan ne bisa zarginsu da hƙar zinare ba bisa ƙa’ida ba.

Da farko dai, jami’ai sun yi hasashen cewa ɓarkewar cuta ce ta yi sandiyar mutuwar matasan.

Wakilin BBC ya ce Rahotanni sun nuna cewa matasan sun rasu ne sakamakon cunkoso da rashin isasshen iska a wurin da ake tsare da su.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai