• Home  
  • Hukumar Jin dadin alhazai ta kasa ta bullo da wani sabon tsarin masauki a Madina
- Labarai

Hukumar Jin dadin alhazai ta kasa ta bullo da wani sabon tsarin masauki a Madina

 Ta umarci maniyyata da cewa za su shafe kwanaki biyar ne kacal a Madina su koma Makka bayan sun ziyarci Masallacin Annabi (S.A.W) da sauran wurare masu tsarki a biranen biyu masu tsarki.

Hukumar Jin dadin alhazai ta kasa ta bullo da wani sabon tsarin masauki a Madina

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta bullo da wani sabon tsari na masauki a Madina.

 Ta umarci maniyyata da cewa za su shafe kwanaki biyar ne kacal a Madina su koma Makka bayan sun ziyarci Masallacin Annabi (S.A.W) da sauran wurare masu tsarki a biranen biyu masu tsarki.

Mataimakin daraktan yada labarai da na hukumar, Alhaji Mousa Ubandawaki, ne ya ba da umarnin a cikin wata sanarwa, inda ya ce wannan umarni zai fara aiki ne daga yau, 8 ga watan Yunin 2023.

Sannan ya ƙara da cewa Sabuwar manufar ta zama wajibi ne biyo bayan korafin cunkoson alhazan Nijeriya a birnin Madina.

Yana da kyau a a sani cewa a karon farko cikin dogon lokaci NAHCON ta bai wa alhazan Nijeriya dari bisa dari damar zuwa Madina.

Sanin kowa ne cewa alhazan Nijeriya na zaune ne a unguwar Markaziyya ta musamman a lokacin zamansu a Madina, matakin da ya sha yaba wa matuka.

Ubandawaki ya kara da cewa, idan ana son a dore da manufofin, to dole ne a rage adadin kwanakin mahajjata a Madina.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai