• Home  
  • Sarkin Musulmi III ya buƙaci ƙungiyar ƙwadago ta janye shiga yajin aiki
- Labarai

Sarkin Musulmi III ya buƙaci ƙungiyar ƙwadago ta janye shiga yajin aiki

Mai alfarma Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli a Harkokin Addinin Musulunci, Alhaji Sa’ad Abubakar na uku, ya yi kira ga ƙungiyoyin ƙwadago da su janye batun yajin aiki da zasu shiga a faɗin ƙasar daga ranar Talata 3 ga watan Oktoba.

Sarkin Musulmi III ya buƙaci ƙungiyar ƙwadago ta janye shiga yajin aiki

Mai alfarma Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli a Harkokin Addinin Musulunci, Alhaji Sa’ad Abubakar na uku, ya yi kira ga ƙungiyoyin ƙwadago da su janye batun yajin aiki da zasu shiga a faɗin ƙasar daga ranar Talata 3 ga watan Oktoba.

Sarkin ya bayyana hakan ne a wajen bude taron shirya bikin cikar ƙasar nan shekaru 63 da samun ‘yancin kai wanda ya gudana a jiya Juma’a a birnin tarayya Abuja.

Ya jaddada buƙatar tattaunawa don nemo mafita kan batutuwan maimakon fara yajin aikin ko don maslahar talakawa.

A ƙarshe ya ce yana mai bayar da shawarar tattaunawa ne saboda yajin aikin ba zai magance matsalolin ƙasar nan ba.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000