Home » Abba Ya Taya Babandede Alhinin Rashin Mahaifiyarsa

Abba Ya Taya Babandede Alhinin Rashin Mahaifiyarsa

by Mubarak Ibrahim Mandawari
0 comment
Gwamnan Kano ya Taya Al'umma Murnar Maulidi

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya miƙa saƙon ta’aziyya ga tsohon Shugaban Hukumar shigi da fici ta Najeriya kuma mamallakin tashoshin talabijin da radio na MUHASA Muhammad Babandede bisa rashin mahaifiyar sa da yayi a ranar Alhamis.

Muhmmad Babandede ya rasa mahaifiyarsa Hajiya Hajara mai shekaru 90 a ranar Alhamis bayan rashin lafiya da tayi a asibitin Malam Aminu Kano.

Cikin saƙon da ya fitar ta bakin mai magana da yawun sa Sanusi Bature Dawakin Tofa, Gwamna Abba ya bayyana Marigayiya Hajiya Hajara a matsayin mace mai tsoron Allah da kiyaye iyakokin addinin musulunci.

Gwamna Abba ya kuma  jinjinawa tsohon Shugaban Hukumar na shigi da fici Muhammad Babandede bisa irin namijin Kokorin da yayi a lokacin da yake shugabancin hukumar.

A ƙarshe yayi addu’ar Allah ya jikanta da rahama, ya kuma bashi ikon jure wannan babban rashin.

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?