Home » An Kama Mai Kai Wa Turji Makamai 

An Kama Mai Kai Wa Turji Makamai 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Rundunar Sojin Operation Fansar Yamma, sun kama wata mata mai shekara 25 a Jihar Zamfara da ke kai wa ƙasurgunin ɗan ta’adda Bello Turji Makamai a jihar Zamfara. 

Dakarun rundunar sojin sun kama matar ne ɗauke da alburusai 764 da bindigogi guda shida.

Wannan bayani na ƙunshe a cikin wata sanarwa da kakakin Operation Fansar Yamma, Laftanar Kanal Abubakar Abdullahi ya fitar.

Ya ce, an kama matar tare da wani abokin tafiyarta ne a ranar Asabar 28 ga watan Disamba, a yankin Badarawa, a Ƙaramar Hukumar Shinkafi jihar Zamfara.

Laftanar Kanal Abubakar Abdullahi ya ce sun samu wannan nasara ne bayan samun rahoton sirri kan safarar makamai a yankin.

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?