Rundunar Sojin Operation Fansar Yamma, sun kama wata mata mai shekara 25 a Jihar Zamfara da ke kai wa ƙasurgunin ɗan ta’adda Bello Turji Makamai a jihar Zamfara.
Dakarun rundunar sojin sun kama matar ne ɗauke da alburusai 764 da bindigogi guda shida.
- Abba Ya Taya Babandede Alhinin Rashin Mahaifiyarsa
- Najeriya Na Iya Samun Tiriliyan 1 Duk Wata A Noman Zogale – Dokta Michael
Wannan bayani na ƙunshe a cikin wata sanarwa da kakakin Operation Fansar Yamma, Laftanar Kanal Abubakar Abdullahi ya fitar.
Ya ce, an kama matar tare da wani abokin tafiyarta ne a ranar Asabar 28 ga watan Disamba, a yankin Badarawa, a Ƙaramar Hukumar Shinkafi jihar Zamfara.
Laftanar Kanal Abubakar Abdullahi ya ce sun samu wannan nasara ne bayan samun rahoton sirri kan safarar makamai a yankin.