Home » Allah ya yi wa sarkin Ebira rasuwa

Allah ya yi wa sarkin Ebira rasuwa

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Allah ya yi wa sarkin Ebira rasuwa

Allah Ya yi wa Mai martaba Ohinoyi na kasar Ebira, Alhaji Ado Ibrahim rasuwa wanda har ila yau shi ne mataimakin shugaban Jama’atu Nasril Islam (JNI) na kasa,

Dokta Ado Ibrahim ya kasance shahararren dan kasuwa wanda ya shafe yawancin rayuwarsa a jahar Lagas kafin ya zama Ohinoyi na kasar Ebira. Ya hau kujerar sarautar Ohinoyi na kasar Ebira bayan rasuwar Ohinoyi Sanni Omolori na gidan Oziada a shekarar 1997.

An haifi marigayi sarkin ne a ranar 7 ga watan Fabrairun shekarar 1929. Ya yi karatun boko da na addini, ya rasu yana da shekaru 94. Za a yi jana’izarsa a yau lahadi  29 ga watan Oktoba, a fadarsa da ke birnin Okene, a Jihar Kogi.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?