Home » Ambaliya Ta Ɗaiɗaita Dubban Mutane A Valeancia

Ambaliya Ta Ɗaiɗaita Dubban Mutane A Valeancia

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Tun bayan faruwar ambaliyar ruwa da tayi sanadiyar rasuwar mutane aƙalla 95 tare da raba wasu da muhallan su, ana cigaba da aikin ceto a garin Valeancia dake ƙasar Sifaniya.

Lamarin ya faru a ranar Laraba 30 ga watan Oktoba na shekarar 2024, inda aka shafe awanni shida ana tafka ruwa babu ƙaƙƙautawa. Wannan ita ce ambaliya mafi muni da aka gani a kasar ta Sifaniya.

Zuwa yanzu dai waɗanda suka rasu sun kai aƙalla mutum 95, a daidai lokacin da ake ci gaba da gudanar da ayyukan ceto.

Daga cikin waɗanda suka rasu akwai ɗan Burtaniya mai shekara 71 bayan an ceto shi a gidansa da ke Alhaurin de la Torre a garin Malaga.

Kawo yanzu dai ruwan ya tsagaita, amma firaiministan ƙasar Pedro Sanchez, ya ce akwai buƙatar mazauna yankin su ɗan dakata a tabbatar da tsayawar ambaliyar.

Hukumomi dai a ƙasar sun ce har yanzu ba a tantance haƙiƙanin mutane nawa suke ɓace ba a sanadiyar ambaliyar.

Mutane da yawa sun yi asarar dukiyoyin su da suka haɗa ababen hawa da gidaje dadai sauransu.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?