• Home  
  • An Bada Hutun Maulidi A Najeriya
- Babban Labari - Labarai

An Bada Hutun Maulidi A Najeriya

Gwamnatin Najeriya ta ayyana ranar Litinin 16 ga watan Satumba, a matsayin ranar hutu ga ma’aikatan ƙasar, domin bikin ranar Maulidin Annabi Muhammad S.A.W.

Gwamnatin Najeriya ta ayyana ranar Litinin 16 ga watan Satumba, a matsayin ranar hutu ga ma’aikatan ƙasar, domin bikin ranar Maulidin Annabi Muhammad S.A.W.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da babban sakatare a ma’aikatar cikin gida ta Najeriya, Dokta Magdalene Ajani ya fitar. 

Ya ce ministan ma’aikatar, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hutun Maulidin a madadin gwamnatin Najeriya.

Sanarwar ta ce, ”Gwamnatin Najeriya na taya al’ummar Musulmin ciki da na waje murnar zagayowar ranar Maulidin”

Ministan ya yi kira ga musulman Najeriya su yi amfani da lokacin bikin Maulidin wajen yi wa ƙasar addu’ar zaman lafiya da ci gaba.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai