An Ga Watan Azumin Ramadan A Ƙasar Saudiyya

Daga: Safiyanu Haruna Kutama 

Kasar Saudiyya ta sanar da ganin jinjirin watan Ramadan na Shekarar 1446 Bayan Hijra a Yau Din nan.

Tashar voice of Afric VOA ta rawaito, za a fara Azumin bana a kasa mai tsarki daga gobe asabar, a matsayin 1 ga watan Ramadana .

Kafar yada labarai ta Haramain Sharifain dake kasar Saudiyya ce ta Sanar da hakan a Sahihin shafinta na Facebook da X wato Twitter.

Dama dai yau Juma’a ne 29 ga Watan sha’aban Kuma ita ranar da mai alfarma sarkin musulmi ya bada Umarnin a fara duban jinjirin watan duban wata a Nigeria.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malaman da aka sace a Kogi

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya