- Babban Labari - Labarai

An Kama Yahaya Bello

Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), ta kama Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, kan zargin karkatar da kuɗaɗe a lokacin gwamnatinsa. Jami’an EFCC sun bayyana cewa suna  yi masa tambayoyi dangane da zarge-zargen da ake masa. Sai dai wasu rahotanni na cewa Yahaya Bello ya je ofishin EFCC ɗin ne […]

Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), ta kama Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, kan zargin karkatar da kuɗaɗe a lokacin gwamnatinsa.

Jami’an EFCC sun bayyana cewa suna  yi masa tambayoyi dangane da zarge-zargen da ake masa.

Sai dai wasu rahotanni na cewa Yahaya Bello ya je ofishin EFCC ɗin ne da kansa ba kamo shi aka yi ba.

Idan ba a manta ba Yahaya Bello, ya shiga wasan ɓuya tsakaninsa da EFCC tun bayan da ya sauka daga mulki.

Duk da zarge-zargen da EFCC ke masa na karkatar da kuɗaɗe a lokacin da yake mulkin Jihar Kogi, Bello ya musanta aikata hakan.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai