Home » An Kama Yahaya Bello

An Kama Yahaya Bello

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), ta kama Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, kan zargin karkatar da kuɗaɗe a lokacin gwamnatinsa.

Jami’an EFCC sun bayyana cewa suna  yi masa tambayoyi dangane da zarge-zargen da ake masa.

Sai dai wasu rahotanni na cewa Yahaya Bello ya je ofishin EFCC ɗin ne da kansa ba kamo shi aka yi ba.

Idan ba a manta ba Yahaya Bello, ya shiga wasan ɓuya tsakaninsa da EFCC tun bayan da ya sauka daga mulki.

Duk da zarge-zargen da EFCC ke masa na karkatar da kuɗaɗe a lokacin da yake mulkin Jihar Kogi, Bello ya musanta aikata hakan.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?