Home » Wutar Lantarki Ta Dawo Jahun Bayan Shekaru 8

Wutar Lantarki Ta Dawo Jahun Bayan Shekaru 8

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Mazauna karamar hukumar Jahun a jihar Jigawa na farin cikin dawowar wutar lantarki, bayan shafe shekaru 8 suna cikin duhu.  

A zantawar mazauna yankin da Kamfanin Dillancin Labarai na NAN a ranar Litinin a Jigawa, sun ce, yaran da aka haifa ƙasa da shekara bakwai, ba su san me ake cewa wutar lantarki a yankinsu ba.

Wani ma’aikacin gwamnati a yankin Malam Muhammed Abdullah, ya bayyana godiyarsa ga sabon shugaban da ƙaramar hukumar bisa yadda wutar ta dawo ƙasa da wata guda da karɓar mulki.

Ya ce, “Mun yi mamakin dawowar wutar lantarki cikin gaggawa, kuma mun yaba da hangen nesa da shugaban ya yi, saboda rashin wutar lantarki ya kori ‘yan kasuwa da dama,”

Wani mai injin niƙa a Jahun Umar Baballe, ya ce rashin wutar lantarki ja tilasta masa haƙura da sana’ar.

Baballe ya ce da farko ya fara amfani da man dizal amma asara ya yi ta tafkawa.

Ya ce dawowar wutar lantarki ya inganta abubbuwa da yawa, hatta ruwan sha ya samu.

A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Jamilu Danmallam ya bayyana cewa daga hawansa kujerar mulkin karamar hukumar ne ya gayyaci masana da su binciki matsalar wutar lantarkin.

Ya ce baban abin da aka gano shine ɓata gari da ke lalata turakun wuta.

Danmallam ya ce, gano haka ne ya hada kai da ‘yan sanda da kungiyoyin agaji don magance matsalar, wanda hakan ya taimaka wurin dawowar wutar.

Danmallam ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa kasancewarsa nagartaccen jagora.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?