• Home  
  • An Karrama Gwamnan Jigawa Kan Habaka Noma 
- Babban Labari - Labarai

An Karrama Gwamnan Jigawa Kan Habaka Noma 

Cibiyar masana hulda da jama’a ta Najeriya (NIPR) ta yi taron karrama gwamannan jihar Jigawa Malam Umar A. Namadi da lambar yabo mafi girma ta cibiyar (DIAMOND PRIZE) bisa zamowarsa gwarzon gwamna a fannin habbaka aikin noma da samar da abinci.

Daga Auwal Hussain Dukawuya

Cibiyar masana hulda da jama’a ta Najeriya (NIPR) ta yi taron karrama gwamannan jihar Jigawa Malam Umar A. Namadi da lambar yabo mafi girma ta cibiyar (DIAMOND PRIZE) bisa zamowarsa gwarzon gwamna a fannin habbaka aikin noma da samar da abinci.

Taron karramawar ya gudana ne a dakin taro na Ahmadu Bello dake babbar sakatariyar gwamnati jihar dake Dutse.

Kwamishinoni sun gabatar da makaloli kan nasarar da gwamnatin jihar ke samu, ciki har da kwamishinan yada labarai na jihar Hon. Sagir Ahmad Musa.

Taron ya samu halartar manya-manyan mutane daga ciki da wajen jihar Jigawa. 

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai