Home » An Karrama Gwamnan Jigawa Kan Habaka Noma 

An Karrama Gwamnan Jigawa Kan Habaka Noma 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Daga Auwal Hussain Dukawuya

Cibiyar masana hulda da jama’a ta Najeriya (NIPR) ta yi taron karrama gwamannan jihar Jigawa Malam Umar A. Namadi da lambar yabo mafi girma ta cibiyar (DIAMOND PRIZE) bisa zamowarsa gwarzon gwamna a fannin habbaka aikin noma da samar da abinci.

Taron karramawar ya gudana ne a dakin taro na Ahmadu Bello dake babbar sakatariyar gwamnati jihar dake Dutse.

Kwamishinoni sun gabatar da makaloli kan nasarar da gwamnatin jihar ke samu, ciki har da kwamishinan yada labarai na jihar Hon. Sagir Ahmad Musa.

Taron ya samu halartar manya-manyan mutane daga ciki da wajen jihar Jigawa. 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?