Home » An Kashe ‘Yan Jarida 68 A 2024 -UNESCO

An Kashe ‘Yan Jarida 68 A 2024 -UNESCO

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Hukumar kula da ilimi, kimiya da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya (UNESCO) ta ce a shekarar 2024 an kashe ‘yan jarida 68 a bakin aiki.

UNESCO ta bayyana cewa shekaru biyu a jere, rayuwar ‘yan jarida da ma’aikatan yada labarai na cikin mummunar hatsari a yankunan da ake fama da rikici.

Darakta Janar a UNESCO Audrey Azoulay ta bayyana cewa wannan shine karo na farko a cikin shekaru goma da aka salwantar da rayuwar ‘yan jarida a bakin aiki da dama haka.  

Ta ce “Samun sahihan bayanai na da mahimmanci kwarai da gaske a duk lokacin da aka samu rikici, domin bayanan za su  taimakawa jama’ar da abin ya shafa, kuma za a  wayar da kan duniya baki daya. 

“Bai kamata ‘yan jarida suna salwantar da rayuwar su a bakin aiki ba.

“Ina kira ga gwamnatoci su tashi tsaye wajen tabbatar da tsaron rayukan ‘yan jarida, bisa ga dokokin kasa da kasa.”

Rahoton na UNESCO ya ce an kashe ‘yan jarida 42 a yankunan da ake fama da rikici a bana, inda aka gano cewa an kashe ‘yan jarida 18 a Falasdinu.

Sauran ƙasashen kuma sune Ukraine, Kolombiya, Iraki, Lebanon, Myanmar, da Sudan.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?