Home » Kaso 40 Na Masu Mutuwa Da Cutar Malariya A Duniya ‘Yan Najeriya Ne _WHO

Kaso 40 Na Masu Mutuwa Da Cutar Malariya A Duniya ‘Yan Najeriya Ne _WHO

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Hukumar Lafiya Ta Duniya (WHO) ta bayyana cewa kaso 30 na masu mutuwa sakamakon zazzabin cizon sauro a duniya ‘yan Najeriya ne. 

Rahoton da WHO ta fitar a ranar Alhamis ya ce Najeriya ita ma ta kai kusan kashi 40% na mace-macen zazzabin cizon sauro a fadin duniya a tsakanin yara ‘yan kasa da shekaru biyar.

A shekarar 2023 kaso 30.9% na wadan da zazzabin cizon sauro a duniya ‘yan Najeriya ne. 

WHO ta bayyana cewa a duk duniya a shekarar 2023, an sami kusan mutane miliyan 263 ne aka kiyasta cewa sun kamu da cutar zazzabin cizon sauro.

Hukumar ta ce tsakanin shekarar 2000 zuwa 2019, adadin masu kamuwa da cutar zazzabin cizon sauro a kowace shekara ya karu kwarai da gaske.

A cewar rahoton na WHO, daga shekarar 2020, adadin masu kamuwa da cutar zazzabin cizon sauro ya karu sosai, inda kaso 89.7% na wadan da suka kamu da cutar suka fito daga Afirka.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?