Home » An Saka Dokar Hana Fita A Mina Jihar Neja

An Saka Dokar Hana Fita A Mina Jihar Neja

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Gwamnan Neja Umar Mohammed Bago, ya saka dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 12 a Minna babban birnin Jihar.

An ɗauki wannan matakin ne sakamakon hare-haren da suka janyo salwantar rayuka.

A jawabin dokar, gwamnan ya ce, an haramta zirga-zirgar baburan ’yan acaɓa da masu Keke Napep daga ƙarfe 6 na yamma zuwa 6 na safe.

Gwamnan ya bayyana hakan a yayin wani taro na musamman da ya gudanar da masu ruwa da tsaki kan sha’anin tsaro da ya ƙunshi sarakunan gargajiya da shugabannin hukumomin tsaro a Fadar Gwamnatin jihar a ranar Talata.

Sai dokar ba ta shafi duk wata buƙatar lafiya ta gaggawa ba, Bago ya ce ba a buƙatar ganin ababen hawa daga lokacin da dokar ta fara aiki.

Ya ce ya ɗauki wannan matakin ne da zummar daƙile matsalar tsaro da babban birnin ke fuskanta.

Bago ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta zuba ido a yayin da marasa son zaman lafiya ke ci gaba da kai hare-hare da kashe mutanen da ba su ji ba kuma ba su gani ba a jihar.

Gwamnan ya umarci dukkan dagatai da masu unguwanni da su tabbatar da ɗaukar bayanan duk wasu baƙi da suka shigo yankunansu.

Haka-zalika, ya yi gargaɗin cewa duk gidan da aka kama yana bai wa ‘yan tada zaune tsaye mafaka ko masu fataucin muggan ƙwayoyi za a rushe shi.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?