• Home  
  • Ana cigaba da hako mutanen da gini ya danne a Sudan
- Kasashen Ketare - Labarai

Ana cigaba da hako mutanen da gini ya danne a Sudan

Ana ci gaba da luguden wuta a biranen Khartoum da ma yankin yammacin Dafur a cewar shaidun gani da ido, duk da yunkurin kawo karshen rikicin da kasashen duniya ke yi.

Ana cigaba da hako mutanen da ɓaraguzan gini ya danne a Sudan

Ana ci gaba da luguden wuta a biranen Khartoum da ma yankin yammacin Dafur a cewar shaidun gani da ido, duk da yunkurin kawo karshen rikicin da kasashen duniya ke yi.

Wani mummunan hari da aka kai ta sama a garin Ombada mai yar tazara da birnin Khartoum ya yi sanadiyar rayukan mutane 5 yayin da wasu 17 suka jikkata.

Masu aikin ceto na ci gaba da neman mutanen da suka makale a ɓaraguzan gine-gine lamarin da ya sa ake ganin adadin wadanda suka mutu ka iya karuwa.

Ya zuwa yanzu, sama da mutum dubu uku ne rikicin Sudan ya sa suka rasa rayukansu, a cewar wata kungiya mai tattara bayanan yaki.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai