Home » Ana cigaba da hako mutanen da gini ya danne a Sudan

Ana cigaba da hako mutanen da gini ya danne a Sudan

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Ana cigaba da hako mutanen da ɓaraguzan gini ya danne a Sudan

Ana ci gaba da luguden wuta a biranen Khartoum da ma yankin yammacin Dafur a cewar shaidun gani da ido, duk da yunkurin kawo karshen rikicin da kasashen duniya ke yi.

Wani mummunan hari da aka kai ta sama a garin Ombada mai yar tazara da birnin Khartoum ya yi sanadiyar rayukan mutane 5 yayin da wasu 17 suka jikkata.

Masu aikin ceto na ci gaba da neman mutanen da suka makale a ɓaraguzan gine-gine lamarin da ya sa ake ganin adadin wadanda suka mutu ka iya karuwa.

Ya zuwa yanzu, sama da mutum dubu uku ne rikicin Sudan ya sa suka rasa rayukansu, a cewar wata kungiya mai tattara bayanan yaki.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?