• Home  
  • Mata Masu Juna Biyu Na Cigaba da Mutuwa a Arewa Ta Tsakiya – WHO
- Lafiya

Mata Masu Juna Biyu Na Cigaba da Mutuwa a Arewa Ta Tsakiya – WHO

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce ana cigaba da samun matsalar mutuwar mata masu juna biyu a lokacin haihuwa jihohin Arewa ta tsakiya.

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce ana cigaba da samun matsalar mutuwar mata masu juna biyu a lokacin haihuwa jihohin Arewa ta tsakiya.

Hukumar dai ta ayyana jihar Neja cikin jihohin da ke fama da wannan matsala sasboda matsalar tsaro, duk kuwa da ƙoƙarin da jami’ai ke yi.

Hukumar ta ce da yawan yaran da aka haifa a wannan yankin ba a yi masu riga-kafi saboda yawan rikicin da ake samu masu alaƙa da rashin tsaro.

Shugabar da ke kula da shiyyar, Dr Asma’i Zeenat Kabir ce ta bayyana hakan a taron hukumar karo na 75 da ya gudana a Minna babban birnin jhar.

Hukumar ta yi kira kan hukumomi da su ƙara zage damtse don bunƙasa harkokin lafiya a yankin.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai