Labarai

Babban Labari

Tinubu ya yi alhinin rasuwar Bamanga Tukur

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana alhininsa kan rasuwar fitaccen ɗan kasuwa kuma tsohon gwamnan tsohuwar Jihar Gongola, Alhaji Bamanga Muhammad Tukur, wanda ya rasu yana da shekara 90 a duniya. A cikin saƙon ta’aziyyarsa, Shugaba Tinubu ya bayyana rasuwar Alhaji Bamanga Tukur, wanda ke riƙe da sarautar Tafidan Adamawa, a matsayin wani giɓi […]

Wasanni

Iñaki Williams ya yi ritaya daga buga wa Ghana ƙwallo

Ɗan wasan gaban Athletic Bilbao, Iñaki Williams, ya sanar da yin ritaya daga buga wa tawagar ƙasar Ghana, Black Stars, ƙwallo. Ɗan wasan haifaffen Bilbao ya koma wakiltar Ghana a shekarar 2022, bayan da ya taɓa buga wasa ɗaya a tawagar ƙasar Spain. Ya wakilci Ghana a gasar Kofin Duniya ta 2022 da kuma ta […]

Babban Labari

Majalisar Najeriya ta dakatar da zuwa Afirka ta Kudu

Majalisar Dokokin Najeriya ta dakatar da wasu ziyarce-ziyarcen aiki zuwa Afirka ta Kudu, tare da cewa za ta kaurace wa duk wasu ayyukan majalisa da za su kasance a Afirka ta Kudu har zuwa wani lokaci. Matakin ya biyo bayan rahotannin kisan kai, hare-hare, tsoratarwa da lalata kadarorin da suka shafi ƴan Najeriya da sauran […]

Babban Labari

An Kama Masu Safarar Miyagun Ƙwayoyi 7 A Jigawa

Rundunar ’Yan sandan Jihar Jigawa ta kama wasu mutane bakwai da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi, tare da ƙwato nau’in ƙwayoyi daban-daban har guda 5,916 da kuma kunshin tabar wiwi guda biyar. Kamen dai ya biyo bayan wasu samame na musamman da rundunar ta gudanar bisa bayanan sirri a wurare daban-daban na jihar, domin […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai