Labarai

Babban Labari

Kotun tarayya ta ƙi sassauta belin El-Rufai yayin da DSS ta kammala gabatar da hujjoji

Kotun tarayya da ke sauraron shari’ar zargin sauraron wayoyi ba bisa ka’ida ba da ake yi wa tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ta ƙi amincewa da buƙatar da aka gabatar na neman sassauta sharuɗɗan belinsa. Alkalin kotun, Mai Shari’a Joyce Abdulmalik, ta bayyana cewa sharuɗɗan beli masu tsauri da aka kafa tun farko za […]

Babban Labari

Mutane sama da 1,000 sun kamu a da cutar Ebola a Congo

Cutar Ebola ta kama sama da mutane dubu daya a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo, yayin da barkewar cutar ta bazu zuwa sansanin ‘yan gudun hijira na uku, sannan ta yi sanadin mutuwar wata yarinya yar kimanin watanni 18. Gwamnatin Kongo ta tabbatar da cewa adadin mutanen da suka mutu ya kai 254. Yaduwar cutar cikin sauri […]

Babban Labari

Ya kamata gwamnatin Najeriya ta rage farashin man fetur – Sheikh Qaribullah

Shugaban ɗarikar Ƙadiriyya na Afirka, Sheikh Qaribullah Sheikh Nasiru Kabara, ya buƙaci gwamnatin Najeriya ta duba yiwuwar rage farashin man fetur domin sauƙaƙa wa al’umma matsin rayuwar da suke fuskanta. Shehin Malamin ya bayyana hakan ne ta bakin wakilinsa, Sheikh Abdulgaffar Nasiru Kabara, wanda ya wakilce shi a taron Qadiriyya Media Connect da aka gudanar […]

Babban Labari

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta karɓi baƙuncin jami’an kwalejin leken Asiri ta Sojojin Nijeriya.

  Rundunar ƴan sandan Jihar Kano ta karɓi baƙuncin jami’an kwalejin leken asiri ta Sojojin Nijeriya da ke Karu a Abuja, a wata ziyara da suka kai hedikwatar rundunar da ke Bompai, domin nazari kan amfani da bayanan sirri wajen dakile rikice-rikice da inganta tsaro. Kakakin rundunar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan […]

Babban Labari

Fira Ministan Birtaniya ya yi murabus

Fira Ministan Birtaniya, Keir Starmer, ya yi murabus daga mukaminsa bayan matsin lamba da ya karu daga jam’iyyarsa ta Labour. Starmer ya sanar da sauka daga kujerarsa ne a cikin wata sanarwa da aka watsa kai tsaye a talabijin a safiyar Litinin. Ya bayyana cewa ya amince jam’iyyar Labour ba ta ganin shi a matsayin […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai