Labarai

Labarai

Kanawa mazauna Abuja sun gudanar da babban taro

Kanawa mazauna Abuja sun gudanar da babban taro Ƙungiyar Kanawa Mazauna Birnin Tarayya Abuja ta gudanar da wani babban taro a ranar Lahadi, wanda ya samu halartar shugabannin ƙungiyar daga ƙananan hukumomin birnin. Shugaban Kanawa Mazauna Abuja Initiative Group, Alhaji Ali Baba, ya ce wannan ne karon farko da ƙungiyar ta gudanar da irin wannan […]

Labarai

Rimingado ya kaddamar da kwamitoci 9 da kan yaki da miyagun kwayoyi a Kano.

Shugaban kwamitin haɗin gwiwar hukumomi ta yaƙi da shaye-shaye da fataucin miyagun kwayoyi a Kano, Muhuyi Rimingado, ya ƙaddamar da kwamitoci tara domin ƙara ƙaimi wajen yaƙi da matsalar miyagun ƙwayoyi a jihar. Rimingado ya buƙaci mambobin kwamitocin da su kasance masu jajircewa, tare da aiki kafada da kafada wajen ganin an cimma manufofin rundunar. […]

Babban Labari

Jami’ar Sule Lamido ta ziyarci tashar MUHASA kan shirin bude sashen koyar da aikin jarida

Wakilai daga Jami’ar Sule Lamido da ke Kafin Hausa sun kai ziyara tashar MUHASA Radio da Talabijin, a wani mataki na ƙoƙarin buɗe sashen koyar da aikin jarida a jami’ar. Farfesa Mustapha Dan Malam ne ya jagoranci tawagar, inda suka gana da shugabanci da ma’aikatan tashar domin tattauna muhimman batutuwan da suka shafi koyar da […]

Kasashen Ketare

Sakataren sojin kasan Amurka zai yi murabus

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito daga Mujallar Wall Street cewa ana sa ran Sakataren Rundunar Sojin Ƙasa ta Amurka, Dan Driscoll, zai yi murabus kafin ƙarshen shekara, bayan watanni ana samun takun-saka tsakaninsa da Sakataren Tsaron Amurka, Pete Hegseth. Mujallar Wall Street Journal ta wallafa rahoton ne bisa bayanan wasu mutane da ke […]

Siyasa

APC ta nada Abdulaziz Yari a matsayin jagoran kamfen na Tinubu

Jam’iyyar APC ta nada tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Abdulaziz Yari, a matsayin Darakta-Janar na Kwamitin Yakin Neman Zaben Tinubu-Shettima a zaben 2027 da ke tafe.  Da take sanar da kafa Kwamitin Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa na 2027 a ranar Asabar, APC ta ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai kasance shugaban kwamitin, Kashim Shettima a […]

Labarai

Tinubu ya taya ‘yar Gombe murnar lasha gasar musabaka ta duniya

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Maryam Ibrahim Dan’Azumi, ‘yar asalin Jihar Gombe murnar lashe gasar musabakar Alqur’ani bangaren mata ta duniya ta King Abdulaziz International Qur’anic Competition da aka gudanar a kasar Saudiyya. Maryam ta zama ta farko a rukunin mata a gasar da aka gudanar a birnin Makkah, inda ta doke sauran […]

Kasashen Ketare

Yadda Ebola ke mayar da yara marayu a Kwango

Wani sabon rahoton da ƙungiyar kula da yara ta Save the Children ta fitar ya ce aƙalla yara 180 a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kwango ne suka rasa uwa da uba ko kuma ɗaukacin masu kula da su sanadiyyar ɓarkewar cutar Ebola tun daga watan Mayu. Hukumomi a lardin Ituri, inda nan ne cibiyar yaɗuwar cutar sun […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai