Labarai

Babban Labari Labarai

Aikin Gyaran Kundin Tsarin Mulkin 1999 Ba Shi Da Wata Manufa Ta Boye : Sanata Barau Jibrin.

A yayin taron sauraron ra’ayoyin jama’a da ake gudanar a Kano, Mataimakin   Shugaban   majalisar   dattawa   kuma  shugaban kwamitin duba kundin tsarin mulki na 1999, Sanata Barau Jibrin, ya tabbatar wa ’yan Najeriya cewa aikin gyaran kundin tsarin mulki da ake gudanarwa ba shi da wata manufa ta ɓoye, kuma yana gudana ne bisa buƙatun jama’a. […]

Babban Labari Labarai

Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Binciken Kwamishina Da Ya Karbi Belin Mai Safarar Kwayoyi

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya kafa kwamitin bincike kan tsaya wa wani da ake tuhuma da safarar miyagun ƙwayoyi a gaban kotu da Kwamishinan Sufuri na jihar, Alhaji Ibrahim Namadi ya yi. Wannan na cikin sanarwar da Babban Daraktan Yada Labaran gwamnan Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Asabar […]

Babban Labari Labarai

Nentawe Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban APC

Kwamitin zartarwa na Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, ya amince da nadin Farfesa Nentawe Yilwalda daga jihar Filato a matsayin sabon shugaban jam’iyyar na ƙasa. An cimma matsayar ne yayin taron kwamitin zartarwar na kasa da ya gudana a Abuja. Taron wanda ke gudana a fadar shugaban ƙasar, ya samu halartar Shugaba Bola Tinubu […]

Babban Labari Labarai

KAROTA Da NDLEA Sun Fara Wayar Da Kai Kan Illolin Shan Miyagun Kwayoyi A Kano

Hukumar Kula da Zirga-Zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano (KAROTA) tare da haɗin gwiwar Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), sun gudanar da taron wayar da kai kan illolin shaye-shaye a cikin al’umma, musamman tsakanin direbobi da matasa masu yawan mu’amala da tituna. An gudanar da taron ne a babban ofishin […]

Babban Labari Labarai

Jami’ar Yusuf Maitama Sule Zata Karrama Aminu Dantata, Ahmad Bamba, Rabi’u Kwankwaso Da Wasu Fitattun Mutane

Shugaban Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta Jihar Kano, Farfesa Mukhtar Atiku Kurawa, ya bayyana cewa jami’ar ta yanke shawarar karrama marigayi Sheikh Ahmad Bamba sakamakon gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban jami’ar tun kafin rasuwarsa. Farfesa Kurawa ya bayyana hakan ne a wata zantawa da ya yi da manema labarai, inda ya ce wannan […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000