Home » Budurwa Ta Sa An Lakaɗawa Malaminta Duka A Kano

Budurwa Ta Sa An Lakaɗawa Malaminta Duka A Kano

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Ana zargin wata ɗaliba a kwalejin kimiyya da fasaha ta jihar Kano, da sa samarin ta su yi wa wani malaminsu mai suna Aliyu Hamza Abdullahi dukan kawo wuƙa.

A ranar Talata, 14 ga watan Janairu, 2025 ne haƙok budurwa ya cimma ruwa in da samarin ta suka samu nasarar yi wa malamin laga-laga.

Budurwar ta sa an yi wa Malamin, wanda shi ne jami’in jarabawar sashen karatu ta duka ne bayan ta zarge shi da ƙin sauya mata sashen abin da take karanta.

Rahotanni sun tabbatar da cewa lamarin ya faru ne bayan da dalibar da ta nuna rashin gamsuwa da kwas din aka ba ta, ta buƙaci a canza mata amma sakamakon jarabawar ta bai kai na kwas ɗin da take so ba.

Jami’in hulda da jama’a na kwalejin, Auwal Ismail Bagwai, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Bagwai ya ce, “Malamin ya samu raunuka a hannunsa yayin da yake kokarin kare kansa.

Ya tabbatar da cewa “Hukumomin tsaro suna bincike akan lamarin kuma a halin yanzu malamin da ya ji rauni yana samun kulawa a asibiti.”

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?