Labarai

Gabatar Da Sabon Marubuci

Muna sanar da abokan hulɗar mu cewa Muhammad S. Ahmad Babban Jami’in Na’ura da ke Sashen Nazarin Labarin Ƙasa a Jami’ar Bayero ta Kano ya zama ɗaya daga cikin masu rubutun sharhi da fashin baki a wannan kafa.

Read more

An Dakatar Da Mamman Osuman Daga Shugabancin ACF

Ƙungiyar Tuntuba Ta Arewa ta dakatar da shugabanta na kasa, Mamman Mike Osuman, sakamakon kalamansa dangane da zaben 2027 da ke tafe. An ruwaito shugaban da aka dakatar a yayin taron majalisar zartaswar kungiyar ACF ta kasa a ranar Larabar da ta gabata yana cewa Arewa za ta marawa dan takarar shugaban kasa da ya […]

Read more

An Kama Ɗan Aljeriya Yana Safarar Makamai A Zamfara

Jami’an ‘yan sandan Najeriya a jihar Zamfara sun kama wani ɗan ƙasar Aljariya bisa zargin safarar manyan makamai.  Bincike ya nuna wanda ake zargin ya jima yana safarar makamai a Jihohin Arewacin Najeriya. Kwamishinan ’Yan Sandan jihar Zamfara, Mohammed Dalijan ne ya bayyana kama mutumin a Gusau, a ranar Talata. Ya ce ’yan sanda sun […]

Read more

CUTAR KWALARA TA SAKE BARKEWA A JIHAR SAKKWATO

Kwalara na daya daga cikin ƙwayoyin cututtuka da suke yaduwa ta hanyar ruwa, ko ta abinci maras tsafta. Kwalara na haifar da amai da gudawa, kuma tana saurin yin kisa idan har ba a ɗauki mataki a kan lokaci ba. Waɗanda cutar ta yi wa tsanani za su yi fama da rashin ruwan jiki wanda […]

Read more