Gabatar Da Sabon Marubuci

Muna sanar da abokan hulɗar mu cewa Muhammad S. Ahmad Babban Jami’in Na’ura da ke Sashen Nazarin Labarin Ƙasa a Jami’ar Bayero ta Kano ya zama ɗaya daga cikin masu rubutun sharhi da fashin baki a wannan kafa.

Malam Muhammad S. Ahmad gogaggen marubuci ne a kafafen yaɗa labarai na ciki da wajen Najeriya. Da ya jima ana yi da su a fagen sharhi akan al’amuran yau da kullum.

Da yardar Allah, za a rika wallafa sharhin Muhammad S. Ahmad akan al’amuran yau da kullum duk ranar Asabar.

Muna sanar da abokan hulɗar mu cewa za su iya tuntubar Muhammad S. Ahmad ya yi musu ƙarin haske dangane da wani rubutu da ya yi ko sharhi ta muhammadsahmad00@ gmail.com

 

 

Post masu alaƙa

Tinubu ya cire ministan kuɗi da na gidaje

An kama mutum 2 a hanyar kai wa ’yan ta’adda harsasai 314

Hukumomi a Nijar sun nemi ƴan ƙasar su yi wa jami’an tsaro uziri