Shugaba Tinubu ya ware makudan kuɗaɗe domin farfaɗo da Arewa
Sugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake ware wasu makudan kudade don sake gina yankin Arewacin Najeriya da ya sha fama da matsalar tsaro.Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu
Sugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake ware wasu makudan kudade don sake gina yankin Arewacin Najeriya da ya sha fama da matsalar tsaro.Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu
Akalla mutum biyu sun mutu sakamakon ruftawar wani bene mai hawa biyu a unguwar Garki da ke tsakiyar birnin tarayyar Najeriya Abuja.
‘Yan sandan farin kaya (DSS) daga yankin Arewa maso Gabashin ƙasar nan ta buƙaci gwamnonin yankin da su mayar da hankali wajen rabon kayan tallafin gwamnatin tarayya domin ɗorewar zaman lafiya a yankin.
Shugaban rundunar sojin sama ta Najeriya, Air Marshal Hassan Abubakar, ya ba da tabbacin cewa Najeriya na sa ran isowar jirage masu saukar ungulu har 18 domin inganta ayyukan rundunar.
Gwamnan jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, ya amince da kashe Naira miliyan ɗari bakwai domin biya wa ɗalibai ‘yan asalin jihar nan su kusan dubu bakwai da ke karatu a jami’ar Bayero kudin makaranta.
Kotun daukaka kara, dake babban birnin tarayya Abuja ta kori karar da Abba Kabir Yusuf ya shigar na neman a yi watsi da hukuncin kotun Sauraren kararrakin zaben karkashin jagorancin mai shari’a Oluyemi Akintan Osadebay da ta zartar a ranar 13 ga Yuli, 2023.
Nasiru El-Rufai ya kasance na kusa da shugaban kasa, Bola Tinubu inda ya shawarce shi kan matakin soji da kungiyar ECOWAS ke son dauka kan Jamhuriyar Nijar
Matan da ke gabatar da shirin ‘Mata A Yau’ a wani gidan talabijin a nan Kano, sun ziyarci shugaban hukumar Hisbah Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa a daidai lokacin da ake tafka muhawara kan wasu kalaman da suka yi, a cikin shirin dangane da batun gaisuwa tsakanin mata da miji.
Sabuwar ministar ma’aikatar yawon bude ido, Misis Lola Ade-John, ta ce za ta yi aiki tare da ma’aikatun gwamnati, hukumomi da sauran masu ruwa da tsaki don mayar da bangaren yawon bude ido ya zama babban hanyar samun kudaden shiga ga Nijeriya.
A wani labarin kuma sababbin ministocin tsaro, Muhammad Badaru Abubakar da Bello Matawalle, suna shan suka da caccaka daga ƴan Najeriya saboda rashin gogewar aiki a ɓangaren da aka ba su.