Kungiyar NLC ta sha alwashin sake tafiya yajin aiki na gargaɗi

Ƙungiyar ƙwadago ta NLC a Najeriya ta sanar da aniyar shiga yajin aikin gargaɗi na kwana biyu a kan matsin rayuwa da ‘yan ƙasar ke ciki sakamakon janye tallafin fetur.
NLC ta ce za ta gudanar da yajin aikin ne a ranakun Talata da Laraba mai zuwa.
A ranar da aka rantsar da shi, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya janye tallafin man fetur, yanayin da ya haifar da tsadar litar man fetur a gidajen mai daga naira 197 zuwa 617.
NLC ta nuna ƙin amincewa da matakin gwamnati da aiwatar da zanga-zanga a faɗin ƙasar.
Shugaba Tinubu ya sha ganawa da ‘yan ƙwadagon a kokarin ganin an cimma daidaito.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr