Labarai

Yan Bindiga Sun Yi Hatsari Bayan Karbar Kudin Fansa

Wasu masu garkuwa da mutane sun yi hatsarin mota a hanyarsu ta zuwa rabon kudin fansar mutanen da suka sace a Jihar Nasarawa. Jami’an tsaro sun kwato bindigogi uku da tsabar kudi Naira miliyan 6.9 daga motar ’yan bingidar bayan hatsarin motar a yankin Garaku, daura da wani shingen bincike na Jami’an Kula da Lafiyar […]

Read more

Hutu Na Je A Landan Ba Asibiti Ba – Akpabio

Shugaban majalisar dattawa ta Najeriya, Sanata Godswill Akpabio ya musanta abin da ya kira raɗe-raɗin da ake yaɗawa cewa yana fama da rashin lafiya. Akpabio ya bayyana haka ne a lokacin da ya sauka a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja da asuban ranar Litinin daga birnin Landan, inda wasu sanatoci da […]

Read more

Amurka Ta Yaba Wa Najeriya Bisa Kama Jagororin Ansaru

Ofishin Jakadancin Amurka a Najeriya ya yaba da kama fitattun shugabannin ƙungiyar Ansaru da jami’an tsaronta suka yi. A ranar Asabar ne gwamnatin Najeriya ta ce jami’an tsaronta sun kama ƴan ƙungiyar ta Ansaru, waɗanda take zargi da kitsa fasa gidan yarin kuje a shekarar 2022 har suka tseratar da wasu fursunoni. Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar […]

Read more

Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Kasa Ta Rasu

Mama Lydia Yilwatda, mahaifiyar shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ta rasu. Mai magana da yawun jam’iyyar APC a Jihar Filato, Shittu Bamaiyi, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a Jos ranar Lahadi. A cewar Bamaiyi, Mama Lydia ta rasu ne da safiyar ranar Lahadi a Asibitin Koyarwa na […]

Read more

Sarkin Zuru Ya Rasu

Sarkin Zuru Manjo Janar Muhammadu Sani Sami II mai ritaya ya rasu yana da shekara 81 da haihuwa. Sakataren yaɗa labarai na gwamantin jihar Kebbi, Ahmed Idris, ya faɗa cikin wata sanarwa cewa sarkin ya rasu ne a wani asibiti da ke birnin Landan ranar Asabar da dare. Sarkin tsohon gwamnan mulkin soja ne na […]

Read more

APC Ta Lashe Zaɓukan Cike Gurbi A jihar Kaduna

Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta lashe duka zaɓukan cike gurbi uku da aka gudanar a jihar Kaduna da ke arewacin ƙasar, kamar yadda hukumar zaɓe ta Inec ta sanar. Sakamakon da aka gudanar a mazaɓar majalisar tarayya ta Chikun/Kajuru ya nuna cewa Felix Bagudu na APC ɗin ya samu ƙuri’a 34,580 kuma ya […]

Read more

APC ta buƙaci a soke zaɓen cike gurbi a Kano

Jam’iyyar APC ta buƙaci Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), da ta soke zaɓen cike gurbi na Shanono/Bagwai da kuma na mazaɓar Ghari a Jihar Kano. Jam’iyyar ta buƙaci a soke zaɓen saboda ta zargi cewar an samu tashe-tashen hankula a yankunan da zaɓen ya gudana. A cikin wata sanarwa da kakakin jam’iyyar […]

Read more

Yadda Aka Kama Yan Dabar Siyasa 288 A Kano

  Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta kama mutum 288 da ake zargin ’yan daba ne a lokacin zaɓen cike gurbi da aka gudanar a jihar. Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce an kama mutanen da makamai masu hatsari, ciki har da bindigogi ƙirar gida, wuƙaƙe da adduna. Ya bayyana cewa an yi […]

Read more