Malam Uba Sani Ya Mayarwa Iyalan Abacha Filayen Da El Rufai Ya Karbe
Gwamnan jihar Kaduna Malam Uba Sani ya mayar wa iyalan tsohon shugaban kasa Janar Sani Abacha filayen su guda 2 da tsohon gwamna Nasir El Rufai ya kwace a lokacin mulkinsa.
Gwamnan jihar Kaduna Malam Uba Sani ya mayar wa iyalan tsohon shugaban kasa Janar Sani Abacha filayen su guda 2 da tsohon gwamna Nasir El Rufai ya kwace a lokacin mulkinsa.
Hukumar Rawa Ta Najeriya (National Troupe of Nigeria) a karkashin jagorancin Kaltume Bulama Gana, FSNA, na shirin wani gagarumin taro domin kaddamar da kirkirarriyar fasahar zamani da zimmar karfafawa yara da matasa guiwa wurin kallo da sauraron wakoki, kade-kade da raye-rayen gargajiya.
Rundunar Sojin Najeriya, ta musanta jita-jitar da ake yaɗawa cewar an kafa sansanin sojojin Faransa a Maiduguri, Babban Birnin Jihar Borno. A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Kaftin Reuben Kovangiya, ya fitar. Kaftin Kovangiya, ya yi ƙarin haske cewa jami’in da aka gani a bidiyon ba sojan Faransa ba ne. Ya […]
Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, ta ce ta kai wani samame mafi girma na yini guda a tarihin kafuwar ta kan wasu da ake zargin masu damfara ne ta kafar intanet, inda ta cafke wasu ‘yan kasashen waje 193 da wasu ‘yan Najeriya 599 a Legas.
Shugabannin Ƙungiyar da ke fafutukar haɗe kan magoya bayan ‘yan siyasa a jam’iyyu daban-daban a Jihar Kano da aka yi wa laƙabi da Kwandon Koli ta kawo ziyarar aiki tashar Rediyo da Talabijin na MUHASA.
An wayi gari da hazo a sassan jihar Kano a safiyar Lahadi, inda ba a iya hango wanda ke sama da mita 500.
A ranar Alhamis ɗin da ta gabata ne rundunar sojin Najeriya ta yi wa manyan hafsoshinta 656 ritaya, wadanda suka shafe shekaru 35 a bakin aiki
Farfesa Mahmood Yakubu, Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), ya ƙaryata jita-jitar da ake yaɗawa cewa ya rasu a wani asibiti da ke birnin Landan.
Dakarun Rundunar Sojin Najeriya ta ‘Operation Fansan Yamma’ sun tarwatsa sansanoni 22 na ‘yan ta’addan Lakurawa a jihar Sakkwato.
Shugabannin Ƙasashen Mali, Nijar da Burkina Faso, sun sake tabbatar da matsayarsu na ficewa daga Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen yammacin Afrika (ECOWAS).