Malam Uba Sani Ya Mayarwa Iyalan Abacha Filayen Da El Rufai Ya Karbe

Gwamnan jihar Kaduna Malam Uba Sani ya mayar wa iyalan tsohon shugaban kasa Janar Sani Abacha filayen su guda 2 da tsohon gwamna Nasir El Rufai ya kwace a lokacin mulkinsa.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewar lauyan iyalan tsohon marigayin shugaban kasar Reuben Atabo ne ya bayyana haka ga manema labarai.

Sanarwar gwamnatin jihar Kaduna da Babban Daraktar ma’aikatar kula da filaye Mustapha Haruna ya gabatar tace, Gwamna Uba Sani ya rubutawa iyalan Janar Abacha wasika wanda aka sanya sunan Mohammed Sani Abacha, yana mai bayyana mayar musu da filayen da kuma gabatar musu da bukatar cewar su je su biya harajin da aka saba karba a hannun su na mallakar filayen.

An ce A shekarar 2022 ne dai tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru El Rufai ya gabatar da sanarwa a jarida ranar 28 ga watan Afrilu inda aka bayyana kwace filayen tare da soke takardun wadanda aka mallakawa a farko.

Post masu alaƙa

Sojojin Najeriya sun daƙile yunƙurin garkuwa da mutane tare da ceto mutum 23

Dan KAROTA da direba ya buge ya gudu Nasiru Abdullahi Mai Jihadi ya rasu ya bar mata 2 da ‘ya’ya 12.

An kama budurwa ‘yar shekara 15 kan safarar miyagun kwayoyi a Delta.