Sojoji Sun Ragargaji Sansanonin Lakurawa

Dakarun Rundunar Sojin Najeriya ta ‘Operation Fansan Yamma’ sun tarwatsa sansanoni 22 na ‘yan ta’addan Lakurawa a jihar Sakkwato.

Hakazalika sojojin sun yi nasarar kashe wasu da dama kuma sun kwato makamai da alburusai.

Mukaddashin babban kwamandan runduna ta 8 kuma kwamandan sashi na 2 na rundunar Fansar Yamma, Birgediya Janar Ibikunle Ajose ne ya bayyana hakan, a lokacin da yake jawabi ga runduna ta musamman da aka tura domin murkushe Lakurawa a jihohin Sakkwato da Kebbi a ranar Juma’a.

Ya ce, idan aka tura wasu rundunar ta musamman, to babu shakka zai kara wa rundunar da ke aiki a yankin ƙwarin gwiwa da kuzari wajen dakile ayyukan ‘yan ta’adda a yankin Arewa maso Yamma baki daya.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda