Home » Ciyaman Ɗin Kabo Ya Saya Wa ‘Yan Gabasawa Filin Maƙabarta

Ciyaman Ɗin Kabo Ya Saya Wa ‘Yan Gabasawa Filin Maƙabarta

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Shugaban ƙaramar hukumar Kabo dake Kano kwamared Lawal Na Jume ya saya wa jama’ar garin Gabasawa filin maƙabarta da aka daɗe ana buƙata a yankin. 

An saya wa jama’ar yankin Gabasawa filin maƙabartar ne da yammacin ranar Alhamis 21 Ga Nuwamba 2024 akan Naira miliyan daya da dubu ɗari biyar, kamar yadda sakataren mulkin ƙaramar hukumar Kabo honorabul Abba Salihu mai wake Garo ya bayyana.

Yayin biyan kuɗin maƙabartar, shugaban ƙaramar hukumar Kabo kwamared Lawal Na Jume ya samu rakiyar mataimakinsa honorabul Kabir Lawal da kuma sakataren mulkin ƙaramar hukumar honorabul Abba Salihu mai wake Garo.

An damƙa filin maƙabartar ne da hannun babban limamin Gabasawa da kuma Dagacin yankin.

Bayan biyan kuɗin maƙabartar, limamin garin da wasu dattawa da aka gayyata domin shaida cinikin sun bayyana farin cikinsu da tallafin filin maƙabartar da suka samu daga shugaban ƙaramar hukumar.

 

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?