Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Na Farko A Tarihinta

 

Crystal Palace ta doke Manchester City da ci ɗaya mai ban haushi a filin wasa na Wembley a ranar Asabar, inda ta lashe Kofin FA karo na farko a tarihinta.

Eberechi Eze ne, ya zura ƙwallo ɗaya tilo tun da aka fara wasan, yayin da mai tsaron ragar Crystal Palace, Dean Henderson ya taka rawar gani a wasan wajen hana Man City zura ƙwallo.

Man City ta rasa damar yin kunnen doki a wasan bayan Omar Marmoush ya kasa cin bugun daga kai sai mai tsaron raga.

Henderson, ya tsallake rijiya da baya, bayan duba VAR kan yiwuwar ko hannunsa ya taɓa ƙwallon a wajen yadi na 18.

Wannan nasara ce ta farko da Palace ta taɓa samu a gasar manyan kofuna cikin shekaru 120.

Man City kuwa, wannan na nuna cewar kakar wasanninta ta bana an yi uwa kwance ɗa kwance, wato ba ta lashe kowane kofi ba, hakan na iya ƙara wa kocinta, Pep Guardiola matsin lamba.

Post masu alaƙa

Babbar alkalin Kano ta rantsar da sabbin alkalan kotunan shari’a su 30

Ba za mu buɗe Hormuz ba sai Amurka ta buɗe tashar ruwanmu – Iran

Jirgin ‘yan cirani ya kife a tekun Libiya