Gobara ta yi ajalin ɗalibai 16 a Kenya

Ɗalibai 16 sun mutu sakamakon wata gobara da ta tashi a makarantar kwana da ke Gilgil a Kenya, kamar yadda wani ɗansanda ya shaida wa manema labarai.

Wasu ɗalibai 74 kuma suna samun kulawa a asibiti bayan raunin da suka ji.

Gobarar da ta faru a makarantar ƴanmata ta Utumishi ta soma ne da sanyin safiyar yau Alhamis lokacin da ɗaliban suke barci, in ji ƙungiyar agaji ta Red Cross a Kenya da kuma ƴansanda.

Ƴansanda sun ce ana aikin ceto sai dai zuwa yanzu hukumomi ba su gano musabbabin gobarar ba.

Ƙungiyar Red Cross a Kenya ta ce masu bayar da agajin gaggawa na wajen domin ba da tasu gudunmawar.

A yayin da yake magana da iyayen ɗalibai da sauran mutanen da suka taru a wajen makarantar, babban jami’in ƴansanda Masoud Mwinyi ya ce lamarin abin tashin hankali ne.

Dama a kan samu tashin gobara a makarantun kwana a Kenya inda a shekarun baya-bayan nan lamari ya janyo mutuwar mutane.

Post masu alaƙa

Ko Ganduje ba zai ce shi ba yarona ba ne — Martanin Kwankwaso ga Abba

Sanata Omo-Agege ya fice daga APC

Kwamishinan ƴan sandan Kano CP Ibrahim Adamu Bakori ya gargaɗi masu yunƙurin tayar da hankalin jama’a lokacin bikin sallah