Gombe: Jam’iyyar APC ta Dakatar da Sanata Amos Bulus Bisa Wani Zargi

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da , sakataren yada labaran jam’iyyar APC na jihar MOSES KYARI, ya sanyawa hannu ranar Asabar a Gombe.

Kyari ya ce jam’iyyar ta kuma dakatar da dan majalisar wakilai Yunusa Abubakar mai wakiltar mazabar Yamaltu-Deba a majalisar dokokin tarayya bisa zargin yi wa jam’iyyar zagon kasa.

Ya ce shugabannin mazabarsu sun dakatar da ’yan majalisar ne bayan an same su da aikata laifukan cin hanci da rashawa a lokacin zaben 2023 a jihar.

Kyari, ya ce shugabannin Unguwar Bambam da ke karamar hukumar Balanga ne suka dakatar da Sanatan.

Kyari, ya ce an kafa kwamitin da zai binciki lamarin inda ya ce kwamitin ya gayyaci Sanatan amma bai iya kare kansa daga zargin ba don haka kwamitin ya ba da shawarar dakatar da shi daga jam’iyyar.

Post masu alaƙa

Atiku ya buƙaci Tinubu ya yi bayanin dalilinsa na ƙin halartar taron UNGA karo na uku a jere

Yan sanda da INEC sun yaba da yadda zaɓen Dawakin Kudu ke gudana a Kano.

An dakatar da shugaban NSCDC a Neja kan mutuwar masu haƙar ma’adanai 37