Gwamnan Kano ya sake amincewa da nada-naden sabbin mukamai a gwamnatinsa

Gwamnan Kano ya sake amincewa da nada-naden sabbin mukamai a gwamnatinsa

Gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya sake amincewa da Sabbin nada-naden sabbin mukamai a gwamnatinsa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Sakataren yada labaran gwamnan Kano Bature Dawakin Tofa ya aikowa muhasa.

Wadanda aka nada sun haɗa da:

 Arc. Ahmad A. Yusuf a matsayin babban sakataren , maikatar tarihi da raya al’adu ta jahar kano.

Sai. Engr. Ado Jibrin Kankarofi, a matsayin mukaddashin manajan director, na hukumar kula da hanyoyi na jahar kano wato KARMA.

Sai kuma Hauwa Muhammad a matsayin mai bawa gwamana shawara na musamaman kan harkokin mata.

Sanarwar ta ce Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf wanda ake wa lakabi da Abba Gida-gida ya taya su murna tare da cewa nadin nasu ya fara aiki ne nan take.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *