Home » Gwamnan Kano ya sake amincewa da nada-naden sabbin mukamai a gwamnatinsa

Gwamnan Kano ya sake amincewa da nada-naden sabbin mukamai a gwamnatinsa

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Gwamnan Kano ya sake amincewa da nada-naden sabbin mukamai a gwamnatinsa

Gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya sake amincewa da Sabbin nada-naden sabbin mukamai a gwamnatinsa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Sakataren yada labaran gwamnan Kano Bature Dawakin Tofa ya aikowa muhasa.

Wadanda aka nada sun haɗa da:

 Arc. Ahmad A. Yusuf a matsayin babban sakataren , maikatar tarihi da raya al’adu ta jahar kano.

Sai. Engr. Ado Jibrin Kankarofi, a matsayin mukaddashin manajan director, na hukumar kula da hanyoyi na jahar kano wato KARMA.

Sai kuma Hauwa Muhammad a matsayin mai bawa gwamana shawara na musamaman kan harkokin mata.

Sanarwar ta ce Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf wanda ake wa lakabi da Abba Gida-gida ya taya su murna tare da cewa nadin nasu ya fara aiki ne nan take.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?