• Home  
  • Gwamnan Kano ya sake amincewa da nada-naden sabbin mukamai a gwamnatinsa
- Labarai

Gwamnan Kano ya sake amincewa da nada-naden sabbin mukamai a gwamnatinsa

Sanarwar ta ce Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf wanda ake wa lakabi da Abba Gida-gida ya taya su murna tare da cewa nadin nasu ya fara aiki ne nan take.

Gwamnan Kano ya sake amincewa da nada-naden sabbin mukamai a gwamnatinsa

Gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya sake amincewa da Sabbin nada-naden sabbin mukamai a gwamnatinsa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Sakataren yada labaran gwamnan Kano Bature Dawakin Tofa ya aikowa muhasa.

Wadanda aka nada sun haɗa da:

 Arc. Ahmad A. Yusuf a matsayin babban sakataren , maikatar tarihi da raya al’adu ta jahar kano.

Sai. Engr. Ado Jibrin Kankarofi, a matsayin mukaddashin manajan director, na hukumar kula da hanyoyi na jahar kano wato KARMA.

Sai kuma Hauwa Muhammad a matsayin mai bawa gwamana shawara na musamaman kan harkokin mata.

Sanarwar ta ce Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf wanda ake wa lakabi da Abba Gida-gida ya taya su murna tare da cewa nadin nasu ya fara aiki ne nan take.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000