Gwamnati ta sa dokar hana fita bayan ɓarkewar zanga-zanga a Neja

Hukumomi a jihar Neja sun ƙaƙaba dokar hana fita a Minna, babban birnin jihar Neja sakamakon zanga-zangar da ta ɓarke.

Mai bai wa gwamnan jihar shawara kan yaɗa labarai, Zayyanu A Salihu ya wallafa sanarwar a shafinsa na Instagram.

Ya ce dokar ta tsawon sa’a 24 za ta soma aiki bayan sallar Juma’a.

Hukumomi sun shawarci jama’a da su mutunta dokar.

Post masu alaƙa

Sai ’yan Najeriya sun sayi litar man fetur N5,000 idan Tinubu ya zarce

Kotu ta dage hukunci kan shari’ar datse yatsa bisa alkawarin naira miliyan 80.

An Kashe Makiyaya 50 An Sace Shanu Sama da Dubu 2 A Kaduna — MACBAN