Gwamnatin Kano na daura auren zaurawa a yau

A yau Juma’a 13 ga watan Oktoba ne gwamnatin jihar Kano ke ɗaura auren mata 1,800 da angwayensu wanda ta ɗauki watanni tana shiryawa.

Tun bayan hawansa mulki ne, Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya sanar da cewa zai yi wa matan da suka nuna sha’awarsu ta shiga shirin auren gata ta hanyar samar musu da dukkan kayayyakin da mace ke buƙata a gidan aure da kuma yi musu walicci.

Hukumar Hisbah a jihar ƙarƙashin jagorancin Sheikh Aminu Daurawa ta ce ta jagoranci kammala matakai biyar cikin bakwai na auren, inda za a ɗaura aurarrakin a masallatai a dukkan ƙananan hukumomi 44 da ke faɗin jihar.

Kamar yadda jami’an hulda da jama’a na rundunar ta Hisbah ya bayyana wa muhasa da wannan safiya, ya ce za a ɗaura auren ne bayan sallar juma’a a Masallacin gidan sarki dake cikin gari da kuma masallacin waje dake unguwar Fagge.

Post masu alaƙa

Babandede Ya Ziyarci Iyalan Hon. Laushi, Ya Ba Su Tallafi

Da Fulani Aka Kama da Wuraren ƙera Makamai a Filato, da War Haka Duniya ta Dauka:-Zagazola Makama

Gwamna Bala Mohammed ya canja sheka daga jam’iyar PDP zuwa jam’iyyar APM