Hukumar Hisba Ta Gana da ‘Yan TikTok

A yau ne hukumar Hisba ta Kano, ƙarƙashin jagorancin Kwamandanta, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ta gana da ‘Yan TikTok a hedkwatar hukumar da ke Sharaɗa.

An shirya ganawar ne domin a sami kyakkyawar jituwa tsakaninsu da Hukumar Hisba, don ƙara inganta tarbiyyarsu.

A yayin ganawar, Daurawa ya yi wa ‘Yan Tiktok ɗin alƙawuran da suka haɗa da ba su jari da aurar da su, har ma da mayar da wasu daga cikinsu makaranta.

A karshe kuma kwamandan ya raba wa kowannensu Naira 2000 a matsayin kuɗin data da kuma na mota.

Manya ‘Yan rawar TikTok ɗin da dama sun samu halartar taron.

Post masu alaƙa

An kashe kwamandojin ’yan bindiga biyu a Katsina

Yan Sandan a Kano sun kama mutane 244, ciki har da 117 da ake zargi da fadan daba.

Ƴansanda sun ƙara tsaurara matakan tsaro a bikin Takutaha, tare da gargaɗin masu yunkurin tada zaune tsaye.