Hukumar Hisba Ta Gana da ‘Yan TikTok

A yau ne hukumar Hisba ta Kano, ƙarƙashin jagorancin Kwamandanta, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ta gana da ‘Yan TikTok a hedkwatar hukumar da ke Sharaɗa.

An shirya ganawar ne domin a sami kyakkyawar jituwa tsakaninsu da Hukumar Hisba, don ƙara inganta tarbiyyarsu.

A yayin ganawar, Daurawa ya yi wa ‘Yan Tiktok ɗin alƙawuran da suka haɗa da ba su jari da aurar da su, har ma da mayar da wasu daga cikinsu makaranta.

A karshe kuma kwamandan ya raba wa kowannensu Naira 2000 a matsayin kuɗin data da kuma na mota.

Manya ‘Yan rawar TikTok ɗin da dama sun samu halartar taron.

Post masu alaƙa

Babandede Ya Ziyarci Iyalan Hon. Laushi, Ya Ba Su Tallafi

Da Fulani Aka Kama da Wuraren ƙera Makamai a Filato, da War Haka Duniya ta Dauka:-Zagazola Makama

Gwamna Bala Mohammed ya canja sheka daga jam’iyar PDP zuwa jam’iyyar APM