Home » Hukumar Jin dadin alhazai ta kasa ta bullo da wani sabon tsarin masauki a Madina

Hukumar Jin dadin alhazai ta kasa ta bullo da wani sabon tsarin masauki a Madina

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Hukumar Jin dadin alhazai ta kasa ta bullo da wani sabon tsarin masauki a Madina

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta bullo da wani sabon tsari na masauki a Madina.

 Ta umarci maniyyata da cewa za su shafe kwanaki biyar ne kacal a Madina su koma Makka bayan sun ziyarci Masallacin Annabi (S.A.W) da sauran wurare masu tsarki a biranen biyu masu tsarki.

Mataimakin daraktan yada labarai da na hukumar, Alhaji Mousa Ubandawaki, ne ya ba da umarnin a cikin wata sanarwa, inda ya ce wannan umarni zai fara aiki ne daga yau, 8 ga watan Yunin 2023.

Sannan ya ƙara da cewa Sabuwar manufar ta zama wajibi ne biyo bayan korafin cunkoson alhazan Nijeriya a birnin Madina.

Yana da kyau a a sani cewa a karon farko cikin dogon lokaci NAHCON ta bai wa alhazan Nijeriya dari bisa dari damar zuwa Madina.

Sanin kowa ne cewa alhazan Nijeriya na zaune ne a unguwar Markaziyya ta musamman a lokacin zamansu a Madina, matakin da ya sha yaba wa matuka.

Ubandawaki ya kara da cewa, idan ana son a dore da manufofin, to dole ne a rage adadin kwanakin mahajjata a Madina.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?