Hukumar Kwastam Ta Naɗa Sabon Kakakinta, Abdullahi Aliyu Maiwada

Shugaban hukunar Kanal Hameed Ibrahim Ali mai ritaya ya bada umarnin nada CSC Maiwada bayan duba nagarta da kuma iya aikinsa shekara da shekaru a hukumar.

Maiwada dai ya taba zama kakakin hukumar na Shiyya ta biyu ta hukumar kwastam dake Kaduna ya kuma rike wannan mukami a jihar Ogun dake arewa maso yamma na tsawon shekaru.

Ya dawo shalkwatar hukumar a shekarar 2020 inda ya zama jami’in hulda dake tsakanin gidan jarida na Kwastam da jami’an kwastam a bangarorin Nijeriya.

Maiwada yayi digirinsa na farko a jami’ar Bayero da ke kano, kuma  a yanzu yana da digiri na biyu guda biyu kuma yana digiri na uku a harkar jarida.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *